Biography / Tarihi

Cikakken Tarihin Halima Atete

Halima Yusuf Atete wacce aka sani da Halima Atete (an haifeta ranar 26 ga watan Nuwamba, 1988) ƴar asalin jihar Borno ce dake Maiduguri, shaharariyar yar wasan Hausa ce kuma mai tsara finafinan, wanda mafiya yawan fina finanta takan fito ne a fim na Annamimanci ko Kishi.

Farkon rayuwa

An haifi Halima Atate a ranar 26 ga watan Nuwanbar shekarar alib 1988, a garin Maiduguri dake Jihar Barno a Najeriya.

Halima Atete tayi makarantar Firamari ta, Maigari Primary School, sanan tatafi makarantar gwabnati ta Yerawa Government Secondary School. Jarumar bata tsaya a iya nan ba ta wace makarantar gaba da Secondary inda ta samo kwalin National Diploma a Shari’a and Civil Low.

Sana’ar Fim

Tauraruwar ta shiga Kamfanin shirya Finafinan Hausa dake Kano a Shekarar 2012,[3] yayin da ta fara shirya Fim dinta na farako mai suna Asalina da uwar gulma[4]. Jarumar ta fito a Finafinai sama da guda Dari da Sittin (160).

Fina-finai

Ga wasu daga cikin finafinan ta;

  • Wata Hudu ND
  • Yaudarar Zuciya ND
  • Asalina (My Origin) 2012
  • Kona Gari 2012
  • Dakin Amarya 2013
  • Matar Jami’a 2013
  • Wata Rayuwa 2013
  • Ashabu Kahfi 2014
  • Ba’asi 2014
  • Bikin Yar Gata 2014
  • Maidalilin Aure 2014
  • Soyayya Da Shakuwa 2014
  • Alkalin Kauye 2015
  • Bani Bake 2015
  • Kurman Kallo 2015
  • Uwar Gulma (Mother of Gossip) 2015
  • Mu’amalat 2016
  • Igiyar Zato 2016

Bayan Fage

Tana da ra’ayin cewa ba ta taɓa kwanciya da furodusa don a bata role ɗin da zata fito a fim ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button